Amfara tattara sakamakon zaɓen jihar Edo

 Tun ƙarfe 2:30 na rana kusan duka rufunan zaɓen da ke ƙananan hukumomi 18 na Edo suka rufe tantance masu zaɓe inda kuma wasu a lokacin suka fara ƙirga ƙuri'un da aka kaɗa.

Sai dai akwai wasu rumfunan zaɓen kayayyakin zaɓe ba su isa da wuri ba, wanda hakan ya sa ba su fara zaɓe da wuri ba.

Tuni wasu rumfunan zaɓen suka ƙirga ƙuri'un da aka kaɗa, inda Jam'iyyu biyu da suka fi shahara na APC da PDP ke nasara.

A yanzu dai an fara kai akwatuna gAmfara tattara sakamakon zaɓen jihar Edoundumomi inda ake tattara alƙaluman zaɓe.

Gwamnan jihar Godwin Obaseki ne ke takara ƙarƙashin Jam'iyyar PDP, sai kuma Fasto Osagie Ize-Iyamu ƙarƙashin Jam'iyyar APC.

Sakamakon farko-farko da ya fara fitowa ya nuna duka 'yan takarar sun lashe rumfunan zaɓensu.


Comments

Popular posts from this blog

𝐍𝐈𝐆𝐄𝐑𝐈𝐀 @60:𝐌𝐔𝐋𝐊𝐈𝐍 𝐒𝐎𝐉𝐀 𝐌𝐀𝐒𝐔 𝐇𝐀𝐋𝐈𝐍 𝐓𝐒𝐈𝐘𝐀 𝐃𝐀 𝐍𝐀 𝐊𝐈𝐑𝐊𝐈

𝑫𝒂 𝒋𝒂𝒌𝒊 𝒂𝒌𝒂 𝒌𝒂𝒊𝒘𝒂 𝑮𝒘𝒂𝒎𝒏𝒂𝒏 𝑩𝒂𝒓𝒏𝒐 𝑯𝒂𝒓𝒊.

Kotu Ta Ba Da Umurnin A Rika Barin Likitocin Alzakzaky Suna Ganawa Da A Duk Sadda Ya Bukaci Hakan.