๐‘พ๐‘จ๐‘ป๐‘จ ๐‘ฉ๐‘จ๐‘ฉ๐‘ฉ๐‘จ๐‘น ๐‘ฒ๐‘ถ๐‘ป๐‘ผ ๐‘ซ๐‘จ ๐‘ฒ๐‘ฌ ๐‘ฒ๐‘จ๐‘ซ๐‘ผ๐‘ต๐‘จ ๐‘ป๐‘จ๐‘ฉ๐‘จ ๐‘ผ๐‘ด๐‘จ๐‘น๐‘ต๐‘ฐ๐‘ต ๐‘จ๐‘ช๐‘ฐ ๐‘ฎ๐‘จ๐‘ฉ๐‘จ ๐‘ซ๐‘จ ๐‘บ๐‘ฏ๐‘จ๐‘น๐‘ฐ'๐‘จ๐‘น ๐‘บ๐‘ฏ๐‘ผ๐‘ฎ๐‘จ๐‘ฉ๐‘จ๐‘ต '๐’€๐‘จ๐‘ต ๐‘บ๐‘ฏ๐‘ฐ'๐‘จ ๐‘ฐ๐‘ฉ๐‘น๐‘จ๐‘ฏ๐‘ฐ๐‘ด ๐‘ฌ๐‘ณ๐’๐‘จ๐‘ฒ๐’๐‘จ๐‘ฒ๐’€

 ๏ปฟKotu ta umarci a ci gaba da shariโ€™ar Ibrahim Zakzaky

ELZAKZAKY

Wata babbar kotu a Kaduna da ke arewacin Najeriya ta umarci a ci gaba da shariโ€™ar da aka kawo gabanta kan jagoran mabiya Shiโ€™a a kasar, Sheik Ibrahim Zakzaky.

Sheikh Zakzaky da matarsa Zeenatu na rike tun a shekara ta 2015 bayan mutuwar mabiyan sama da 300 a wata arangama da jamiโ€™an tsaro a garin Zaria.

Sojoji sun ce sun bude wa mabiyan wuta ne a matsayin martani bayan sun yi kokarin kai wa ayarin motocin babban hafsan sojin kasar hari.

A shekara ta 2019 aka haramta kungiyar bayan shafe tsawon watanni na zanga-zanga da rikici da jamiโ€™an tsaro

Lauyan Zakzaky, Mr Femi Falana ya bukaci kotun tayi watsi da tuhumar da ake wa shugaban โ€˜yan shiโ€™ar.

Sai dai alkali kotun ya ce hakan ba mai yiwuwa ba ne saboda bai gama sauraron gundarin karar da aka shigar ba balantana ya yanke hukunci.

Sannan Elzakzaky bai amsa tuhume-tuhumen da ake masa ba.

Elzakzaky da matarsa sun musanta zarge-zargen da ake musu.

Alkalin dai ya tsayar da Nuwamba a matsayin watan ci gaba da sauraron karar.๏ปฟ๐‘ฒ๐’๐’•๐’– ๐’‚ ๐’‹๐’Š๐’‰๐’‚๐’“ ๐’Œ๐’‚๐’…๐’–๐’๐’‚ ๐’•๐’‚๐’ƒ๐’‚๐’…๐’‚ ๐‘ผ๐’Ž๐’‚๐’“๐’๐’Š๐’ ๐’„๐’Š๐’ˆ๐’‚๐’ƒ๐’‚ ๐’…๐’‚ ๐’”๐’‰๐’‚๐’“๐’Š'๐’‚๐’“ ๐‘ฌ๐’๐’›๐’‚๐’Œ๐’›๐’‚๐’Œ๐’š


Comments

Popular posts from this blog

๐๐ˆ๐†๐„๐‘๐ˆ๐€ @60:๐Œ๐”๐‹๐Š๐ˆ๐ ๐’๐Ž๐‰๐€ ๐Œ๐€๐’๐” ๐‡๐€๐‹๐ˆ๐ ๐“๐’๐ˆ๐˜๐€ ๐ƒ๐€ ๐๐€ ๐Š๐ˆ๐‘๐Š๐ˆ

YANDA AKE RUBUTA LABARI

JIRGIN RUWAN ANNABI NUHU DA AMURIKA TA KERA A SHEKARAR 2018