'๐˜๐š๐ง ๐ฌ๐š๐ง๐๐š ๐ฌ๐ฎ๐ง ๐ก๐š๐ซ๐›๐ž ๐ฆ๐š๐ข ๐ณ๐š๐ง๐ ๐š ๐ณ๐š๐ง๐ ๐š ๐ก๐š๐ซ ๐ฅ๐š๐ก๐ข๐ซ๐š ๐š ๐ฃ๐ข๐ก๐š๐ซ ๐ค๐š๐ญ๐ฌ๐ข๐ง๐š.

 ๏ปฟ๏ปฟKashe-kashe: Ana zargin โ€˜Yan Sanda da kashe mai zanga-zanga a Jihar Katsina.


๐‘ซ๐’๐’Ž๐’Š๐’ ๐‘จ๐’Š๐’Œ๐’๐’Ž๐’‚๐’๐’‚ ๐’…๐’‚ ๐’๐’‚๐’ƒ๐’‚๐’“๐’– ๐’๐’‚ ๐’ˆ๐’‚๐’”๐’Œ๐’Š๐’š๐’‚ ๐’…๐’‚๐’ˆ๐’‚ ๐’š๐’‚๐’๐’Œ๐’–๐’๐’‚๐’ ๐’Œ๐’– ๐’”๐’‚๐’Š ๐’‚ ๐’•๐’–๐’๐’•๐’–๐’ƒ๐’†๐’Ž๐’– ๐’•๐’‚

Mutanen Garin Jibiya sun fita zanga-zanga a kan kashe-kashen da ake ta yi.

 Mazauna garin sun ce an yi kwana da kwanaki ana kai masu hari a Katsina - Tun ba yau ba, ana ta fama da matsalar rashin tsaro a Jihar Shugaban kasar An rasa mutum daya daga cikin mazauna garin Jibiya da su ka shirya zanga-zangar

 a sanadiyyar matsalar rashin tsaro da ke addabar yankin na jihar Katsina. 

Jaridar Daily Trust ta fitar da rahoto a jiya cewa alโ€™ummar Jibiya sun yi zanga-zanga domin nuna rashin jin dadin abin da ke faruwa na yawaitar kashe-kashe. 

Wajen wannan zanga-zanga, an harbe wani mutumi, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa. 

Rahotanni sun ce, jami'an tsaro sun kama mutane akalla 43 a jiyan Ana zargin dakarun โ€˜yan sandan Najeriya da aka tura su lafar da wannan zanga-zanga ne su ka harbi wannan Bawan Allah a ranar Litinin, 28 ga Satumba, 2020. 

โ€˜Danuwan marigayin wanda ya bayyana sunansa da Abdulhadi, ya yi magana da โ€˜yan jarida yayin da ya ke kuka, ya ce โ€˜yan sanda sun kashe masa โ€˜dan'uwa. โ€œKanina ne, an kashe shi.โ€ Inji Abdulhadi. 

Wani mutumi da ya fito daga kauyen Daddara, mai suna Falalu Abba, ya bayyana cewa dole ta sa talakawan yankin su ka fita zanga-zanga domin nuna bacin ransu. "A ranar Lahadi, kwana 39 kenan a jere, kullum sai an kai hari. Idan aka kira jamiโ€™an tsaro, sai su ki zuwa mutane sun gaji don haka su ka fito zanga zangar lumana don nunawa duniya halin da suke ciki"

Comments

Popular posts from this blog

๐๐ˆ๐†๐„๐‘๐ˆ๐€ @60:๐Œ๐”๐‹๐Š๐ˆ๐ ๐’๐Ž๐‰๐€ ๐Œ๐€๐’๐” ๐‡๐€๐‹๐ˆ๐ ๐“๐’๐ˆ๐˜๐€ ๐ƒ๐€ ๐๐€ ๐Š๐ˆ๐‘๐Š๐ˆ

YANDA AKE RUBUTA LABARI

JIRGIN RUWAN ANNABI NUHU DA AMURIKA TA KERA A SHEKARAR 2018